Main menu

Pages



 Falalar fadar La Haula Wala Quwwata Illa Billah!

Sayyiduna Abu Musal Ash'ariy (Allah ya yarda dashi) yace "Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata gareshi) yace mun "KACE LA HAULA WALA QUWWATA ILLA BILLAH DOMIN HAKIKA ITA TASKA CE DAGA TASKOKIN ALJANNAH".



To kunga ashe kenan yawaita fa'darta zai iya zama dalilin samun waccen taskar ta lahira, tare da rahamar Allah. Sannan kuma ya wadata mutum tun daga nan duniya.



Mak'hul (rah) daya daga cikin magabata na kwarai yace "Duk wanda yace 'LA HAULA WALA QUWWATA ILLA BILLAHI WALA MANJAA MINAL LAHI ILLA ILAIHI' to Allah zai toshe masa kofofin abubuwan chutarwa har guda saba'in, mafi Qankantarsu ita ce talauci.



To ashe kenan duk wanda ke neman budi da yalwar arziki, ko samun ciniki mai albarka a kasuwancinsa, ko daukaka awajen aikin Gwamnati to ya yawaita fa'din wannan zikirin tare da gaskatawa azuciyarsa. In shaAllah zai samu biyan bukatarsa.



Acikin wata riwayar kuma aka ce "Duk wanda ya fa'di LA HAULA WALA QUWWATA ILLA BIL LAHI, zata zamo masa maganin chututtuka chasa'in da tara. Mafi sauki daga cikinsu shine baqin ciki.



To ashe kenan duk wanda Makiya suka sashi gaba, ko baqin ciki ya dameshi, ko kuma wata chuta acikin jikinsa, ko larura irin ta jinnu, idan ya yawaita La haula in shaAllah zai samu lafiya.



Manzon Allah (saww) ya kasance yana cewa "KU YAWAITA DAGA SHUKE-SHUKEN ALJANNAH - (WATO) LA HAULA WALA QUWWATA ILLA BILLAH".



Kuma Manzon Allah (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) ya kasance yana cewa "Duk wanda yayi wa ni'ima, Kuma yake bukatar ni'imar ta wanzu, to ya yawaita fa'din La haula wala Quwwata illa bilLah".



Wato idan Allah ya baka wata ni'ima ta duniya, kamar arzikin 'Ya'ya ko Mata ko dukiya ko abin hawa, ko daukaka atsakanin mutane, to idan ka yawaita La haula Allah zai kiyayeka daga sharrukan mahassada da makiya da kuma duk wani abinda zai janyo maka gushewarta.



Kuma Manzon Allah (saww) yace "Duk wanda maqiya suka kamashi, kuma bashi da mai Qwatarsa to ya rika fa'din La haula Wala Quwwata illa Bil Lah'.



Aufu bn Malik Al-Ashja'ee (rta) yace "Yayin da abokan gaba suka kamani, na yawaita fa'dinta sai sasarin da suka daureni dashi ya yanke ya zube qasa. Na fito daga garin nasu har na kore rakumansu na taho na shigo garinmu dasu".

Comments