Main menu

Pages

YADDA HADIZA GABON TA KUNNO WUTAR RIKICI TSAKANIN ABDUL AMART DA RARARA

 



Rikicin da Hadiza Gabon ta ballo tsakanin Abdul Amart da Rarara a dandalin ta na YouTube.


Fitaccen mai bada umarni kuma babban darakta a masana’antar kannywood shugaban kamfanin Abnur Entertainment Abdul Amart Mai Kwashewa yayi bayani game da rayuwar sa da yadda ya samo sunan sa na Mai Kwashewa.




Daraktan Yayiwa mawaki Dauda Kahutu Rarara raddi ne game da batun da Rararan Yayi kwanakin baya na cewa Amart din yaron sa ne Rarara ya furta hakan ne a Shirin Gabon Talk Show wanda jaruma Hadiza Gabon ke gudanarwa a dandalinta na YouTube sai Amart ya karyata batun ya kuma bayyanawa duniya su ne suka fito da Mawaƙi Dauda Kahutu Rarara har duniya ta San shi




A lokacin da yake amsa tambaya Yana Mai cewa Sunana Abdul Amart duniya ta sannami kafin asan Rarara wanda a baya Dauda Rarara din yana yin bidiyo ne tare da ‘Yan chamama Kuma bashi da alakar sanin wasu jaurumai a masana’antar Kanywood shine ya Nemi Kulla alaka Damu a lokacin da mukayi wakar laima ta yage ya rokoni in Saka muryarsa.




Rarara Bai ta ba bani kudi munyi film ba a cewar Amart.


Ana zargin Dauda Rarara da Abdul Amart suna da wata kullalliya Kuma wasu na ganin hakan na da nasaba da gwamnatin jihar Kano.

Ga video kuji yadda firan ya kasance


Comments