Main menu

Pages

    

 FA'IDODIN SADAQAH 

                    **********************

Ya kai 'Dan uwa Musulmi!! Ya ke 'Yar uwa Musulma!! Shin ko kun san cewa sadaqah tana da Mutukar amfani arayuwar 'Dan Adam? 


Bari kuji wasu daga cikin fa'idodin dake cikinta : 


1. Sadaqah wata Qofa ce daga kofofin samun shiga Aljannah.


2. Acikin dukkan ayyukan lada, Sadaqah tana daga sahun gaba. Kuma mafificiyar sadaqah ita ce "Ciyar da abinci domin Allah".


3. Sadaqah tana inuwantar da Ma'abotanta aranar Alqiyamah, Kuma tana 'Yantar dashi daga shiga Wuta. (Gwargwadon yawan sadaqarka, shine gwargwadon ni'imar da zaka shiga aranar Alqiyamah). 


4. Sadaqah tana bushe fushin Ubangiji. (Allah yana son masu yinta, don haka ba zai yi fushi da kai ba).


5. Sadaqah tana kiyaye mutum daga Azabar Qabari. 


6. Sadaqah ita ce mafificiyar kyautar da zakayi ma Mamacinka. 


7. Sadaqah, Ubangiji ne ke rainonta har sai ranar Alqiyamah za'a nuna maka ladanta. 


8. Sadaqah tana tsarkake zuciya daga Qazantar nan ta rowa da kyashi. 


9. Sadaqah tana janyo maka soyayyar Allah da soyayyar Mala'ikunsa da Soyayyar bayin Allah.


10. Sadaqah tana janyo maka ninninkuwar ladan ayyukanka. 


11. Sadaqah tana janyo maka hasken fuska aranar Alqiyamah. 


12. Sadaqah tana janyo maka farin ciki anan duniya da kuma lahira. 


13. Sadaqah tana zama dalilin yayewar damuwarka. Kuma tana kiyayeka daga bakin ciki akan abinda ya wuce. 


14. Sadaqah tana kiyayeka daga Firgita aranar Alqiyamah. 


15. Sadaqah tana janyo kankarewar zunubanka, da kuma gafarar laifukanka. 


16. Sadaqah tana janyo ma masu yinta su samu kyakywar cikawa da imani aranar Mutuwarsu. 


17. Sadaqah tana sanya Mala'ikun Allah su rika yi maka addu'ar alkhairi. 


18. Masu yin sadaqah suna daga cikin mafifitan mutane awajen Allah. 


19. Sadaqah tana sanya albarka acikin dukiyarka. Sannan ta tsare dukiyarka daga kowacce irin asara. 


20. Sadaqah tana da albarka. Kuma da wanda ya fitar, da wanda aka wakilta ya bayar, da wanda ya mika, da wanda ya rarraba duk suna cikin ladanta. 


21. Ma'abocin yawaita sadaqah, yana da alkawarin samun lada mai yawa tare da babban sakamako awajen Ubangijinsa. 


22. Yana daga cikin siffofin masu tsoron Allah, zaka iske suna ciyar da dukiyarsu domin Allah, 


23. Sadaqah tana daga cikin manyan alamomin Kyauta da karamci. 


24. Sadaqah babbar dalili ce wajen samun karbuwar addu'o'inka, da yayewar bakin cikinka. 


25. Sadaqah tana kiyaye masu yinta daga afkawa cikin bala'i. 


26. Sadaqah sau daya (in dai an yita domin Allah) tana toshewa kofofi saba'in na Musibu da miyagun abubuwa tun anan duniya. 


27. Sadaqah tana Qara maka tsawon rai da albarkar rayuwa da albarkar dukiya. 


28. Sadaqah tana janyo maka samun nasara tare da taimakon Ubangiji acikin dukkan abinda kasa agabanka. 


29. Sadaqah tana sanyawa ka samu gagarumar nasara akan Maqiyanka da mahassadanka. Kuma kaidinsu ba zai cuceka ba. 


30. Idan wani ciwo yana damunka har ka rasa maganinsa, to yawaita sadaqah. In sha Allah ita Sadaqah magani ce, waraka ce, kuma kariya ce daga dukkan cututtuka. 


31. Sadaqah garkuwa ce daga sharrin 'barayi, ko gobara, kuma tana kiyaye masu yinta daga mummunar cikawa. 


32. Sadaqah ladanta yana tabbatuwa awajen Allah. Koda dabbobi kayi wa sadaqar, ko tsuntsaye, ko Qwaruka. 


33. Babbar sadaqar da zaka fara gabatarwa ayanzu, ita ce kayi "sharing" (wato ya'da) wannan rubutun daga Zauren Fiqhu ba tare da goge koda harafi guda daga ciki ba. 


Idan kayi haka da niyyar sadaqah, to duk wanda ya gani ya karanta kaima kana da lada akansa. 

ZAUREN FIQHU.



JARRABAWA CE DAGA UBANGIJI


DUK LOKACIN DA KA SHIGA TSANANI A RAYUWA KAR KA MANTA DA ABUBUWAN NAN


 Ka tuna cewa Jarrabawa ce daga Ubangijinka, wanda yafi kowa Sonka da Kaunarka.


 Ka tuna cewa Ubangijinka yayi maka haka ne don ya Kankare maka Zunubanka, ko kuma ya daukaka maka darajarka.


Ka tuna cewar rungumar Qaddara

kowacce iri, yana daga cikin Ginshikan Imaninka. Gwargwadon yadda kake rungumar Qaddara, gwargwadon haka imaninka yake.


Ka tuna cewa an jarrabi Annabawa da Manzanni da Salihan bayin Allah

wadanda suka zo kafin ka.


Babu wani Annabin da ya rayu salun alun babu wata jarrabawa a rayuwa da Allah ya dora masa, 


Annabi Ayyuba ga kudi ga Annabta, amma babu lafiya, 


Annabi Yakub ga 'ya'ya ga Annabta amma babu kudi, 


Annabi Ibrahim ga Annabta, ga daukaka amma kuma mahaifin sa yana bashi matsala, 


Annabi Nuhu ga imani ga arziki amma matar sa da 'dansa sune babbar matsalar sa a

rayuwa.

.

Asiya Bintu Mazaahim, ga kudi ga daukaka, ga imani, amma ga kafirin miji "Fir'auna", 


Annabi Yusuf ga kudi, ga kyau, ga Annabta amma babu uwa da uba a tare dashi, ga rayuwar gidan yari, ga sharrin Mata.

.

Annabi Muhammad (S.A.W) ga Annabta, ga kyau, ga dimbin magoya baya amma babu wadatan kudi, 


toh idan har zaka rinka bata rai kana fushi akan wasu matsaloli a rayuwa toh da sauran ka a imani, idan har Annabawa basu zauna haka kawai ba duk da tsoron Allah su, da bautan su, toh kai a suwa? ni a suwa?.

.

Dan haka kada ka rinka saka wa ranka cewa wai a rayuwa akwai wani lokacin da zai zo baka da matsala, ba za'a yi haka ba kuma

ba a taba yi ba, in dai kayi imani da Allah.

ka duba da kyau kaga wani ikon Allah a cikin mutane wani Allah yakan bashi lafiya amma sai a hana shi kudi ko arzikin da zai

rinka walwala dasu, rashin kudin nan sai ya rinka 'daga masa hankali.

.

Wani kuma sai Allah ya bashi kudi amma sai a hana shi lafiyan da zai ji dadin kudin, wani sai Allah ya bashi 'ya'ya masu albarka amma

sai a bar shi babu wadata, 


wata sai Allah ya jarrabe ta da miji mai arziki amma kuma baya nuna ya damu da ita, baya daukar ta da muhimmanci, tana zaune ne kawai domin biyayya da hakuri,


 ba dan tana jin dadi ba, Sai ta rinka tunanin da ace talaka ta samu wanda zai damu da ita, ya so ta ya kauna ce ta, da tayi farin ciki, 


wata Kuma tana chan

tana tunanin ita da me kudi ma ta samu da ta huta, a yayin da wata take auren mai kudin amma tana Allah wadai da kudin tunda baya kula da ita.

.

Dan haka kada kace zaka rayu babu jarrabawa, idan jarrabawar tazo ka roki Allah ya fitar da kai lafiya kawai.


Ya Allah ka yaye mana dukkan Tsanani don son da mukewa Annabi

Muhammad SAW.



Comments