Main menu

Pages

KWANA 2 YA RAGE, A GOGE MANHAJAR TIKTOK IN HAR BA A SASANTA BA

 


Kwanaki kadan ya rage, a sheqe manhajar TikTok

Wani matashin yaro da yayi suna a kafar manhajar Tiktok mai suna abis_fulani shine ya fito da wannan labarin a shafinsa na tiktok.


Wanda daman dai a arewacin Nigeriya idan wannan hukunci ya yiyu zasuji matukar dadi duba da irin yadda ake fitsara da nuna tsiraici yayi yawa sosai ga yayan musulmi.


Wanda matashin yaron abis fulani yayi wani gajeren bidiyo inda yake cewa.



"Kwana hudu ya rage kowa yasan inda dare kasar amerika ta baiwa kamfanin google masu play store da apple store da su cire manjahar titkok kam kam a manhajar dinsu.


Kowa yasani kamfanin tiktok kamfanin china ne sa’a nan kowa ya sani kamfanin google da apple store kamfanin amerika ne wanda wannan karatun ba sai an maimaita shi kowa yasani kasar China da amerika ba’a ga maciji ma’ana ba’a shiri.


Sa’a nan kowa yasan a halin yanzu kamfanin tiktok ya janyewa kamfanin facebook da Instagram kasuwa domin kuwa yanzu Instagram suna so su mayar da manhajar su kamar ta tiktok videos kawai za’a ringa dorawa sannu sannu shine abinda suke so suyi”.


Abis fulani yayi bayyani sosai akan wannan badakalar inda zaku saurari cikowar bayyin a cikin ga shi nan kasa.


Kunga kenan yau kwana 2 da yin wannan video nashi, kenan yau saura kwana 2 kacal ya rage. Muna fatan zasu sasanta tsakaninsu (America da China). 

Ku Kalli Karin bayanin daga bakinsa.



Comments